![Babu inda nace nafi ‘Yan Najeriya Shan Wahalar Tsadar Rayuwa, Amma ina Fatan Matsalar ta Zama Tarihi -Dangote, HOTPEN](https://hotpen.net/wp-content/uploads/2024/02/images-2-7.jpeg)
Daga Wakilinmu
Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya nisanta kansa da wani labari da ake yadawa a kafafen sada zumunta na zamani cewa yafi ‘yan Najeriya shan wahalar tsadar rayuwa.
Aliko Dangote ya tabbatarwa da ‘yan kasa cewa, wasu ne suka dauki nauyin yada labarin domin bata masa suna a daidai lokacin da ‘Yan Najeriya ke cikin halin ‘kaka na kayi’ saboda wahalhalun da ake fama da su .
Sanarwar ta nemi ‘Yan kasar nan da su yi watsi da labarin, inda Dangote yayi fatan kawo karshen matsalar da ake ciki a Najeriya.
“Duk abinda ya shafi yan Najeriya ya shafemu”, inji Sanarwar.
Dangote ya kara da cewa, ”an kawo maganar faduwar darajar Naira da sayen kaya da Dala ne domin cimma wasu bukatu na kashin kai bukatun da ba su samu damar biya ba a baya.”
Kamfanin Dangote na sarrafa siminti da takin zamani da kuma tatar man fetur. A bangaren kayan abinci kuma, Kamfanin na sarrafa sikari, gishiri da kayan dandanon girki ne kadai.
“Mu ma muna siyan muhimman kayan abinci a kasuwa kamar yadda kowa ke siya don amfanin kanmu da kuma bayarwa wajen ciyar da al’umma.” Dangote.
Shugaban kamfanin yayi mamakin yadda ake neman haddasa sabani tsakanin kamfanonin Dangote da bangaren gwamnatin tarayya, inda yace shi dan kasuwa ne ba dan siyasa ba, don haka babu inda yayi maganar kalubalantar Gwamnatin tarayya.
“Kamfaninmu ya kasance me bin dokokin kasa a koda yaushe tare da neman sauki ga al’umma da fatan alheri.”
Saboda haka, sanarwar ta nemi ‘yan Nijeriya su guji daukar sakon da yake ba daga kamfani yake kai tsaye ba, tare da yada rade-radi da jita-jita.